1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Senegal: Kotun tsarin mulki ta soke kudirin dage zabe

February 16, 2024

Kotun tsarin mulkin Senegal ta soke kudirin dage zaben shugaban kasa na wannan shekara wanda ya haifar da gagarumin rikicin siyasa mafi muni a tarihin kasar.

https://p.dw.com/p/4cSaZ
Senegal I Wahlen -  Macky Sall
Hoto: Ngouda Dione/File Photo/REUTERS

Kotun tsarin mulkin ta ce kudirin dokar da majalisar dokoki ta amince da shi na dage zaben zuwa watan Disemba ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar da ke Yammacin Afrika.

Babbar kotun da ke birnin Dakar ta kuma soke kudirin dokar da shugaba Makcy Sall ya dauka na yin gyaran fuska ga jaddawalin zaben a daidai lokacin da ya rage makonni uku a gudanar da shi, sai dai amma ta ce saboda jinkirin da aka samu na rashin gudanar da zaben a ranar 25 ga wannan wata na Fabarairu, hukumomi su gaggawa tsayar da sabon jadawalin zaben shugaban kasar.

Karin bayani: 'Yan sandan Senegal sun tarwatsa masu zanga-zanga a Dakar

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Macky Sall ta fara sako fursunonin siyasa domin samar da masalaha ga rikicin siyasar da ya kunno kai a Senegal.